Ana fargabar mutuwar mutane da dama a hatsarin jirgin ruwa a jihar Niger

Akalla kusan mutane 100 ake fargabar sun mutu a wani Hatsarin jirgin ruwa a jihar Niger.

Hukumar bayar da agajin gaggawa ta jihar Niger ta ce hatsarin ya faru ne a karamar hukumar Borgu ta jihar ranar Litinin da rana.

Abdullahi Baba Arah darakta janar na hukumar ya ce jirgin ya taso ne daga kauyen Dugga Mashaya a mazabar Dugga inda ya nufi kasuwar Wara dake jihar Kebbi.

Baba-Arah ya ce jirgin na ɗauke sa fasinja da aka ƙiyasta cewa za su kai 100 tare da kayayyaki da suka haɗa da hatsi da kuma wasu kayayyakin.

A cewarsa hukumar bata iya gano yawan mutanen da suka mutu ba ko kuma suka tsira a hatsarin.

Ya kara da cewa ana cigaba da aikin nema da kuma ceto mutanen tsakanin ma’aikatan hukumar dana karamar hukumar da kuma mutanen yankin da suka Æ™ware a yin iyo.

More News

Ƴan sanda sun kama mutane 50 kan rikicin da ya faru a wata kasuwa a Lagos

Rundunar Æ´an sandan jihar Legas ta kama mutane sama da 50 da ake zargin suna da hannu rikicin da ya faru a kasuwar Ile...

Ƴan Sanda sun kama wanda ya shirya kai harin jirgin ƙasar Abuja-Kaduna a shekarar 2022

Rundunar ƴan sandan Najeriya ta ce jami'anta sun kama wani mutum mai suna Ibrahim Abdullahi wanda ake zargi da kitsa harin jirgin ƙasar da...

Ƴansanda sun kama wanda ya kitsa harin da aka kai wa jirgin ƙasa a Kaduna

Rundunar ‘yan sandan Najeriya a ranar Alhamis, ta sanar da kame wanda ake zargin ya shirya harin da aka kai a jirgin ƙasan Abuja-Kaduna...

Sojoji Sun Ceto Mutane Daga Hannun Masu Garkuwa Da Mutane A Filato

Dakarun rundunar Operation Safe Haven dake aikin tabbatar da tsaro a jihar Filato da wani É“angare na jihar Kaduna sun samu nasarar ceto mutane...