Ana duba yiyuwar kai shugaban kungiyar ƙwadago ta NLC asibitin kasar waje

Kungiyar Kwadago ta Najeriya NLC ta ce tana tattaunawa kan duba yiyuwar kai shugaban kungiyar Joe Ajaero ƙasar waje domin a duba lafiyarsa.

Benson Upa mai magana da yawun kungiyar shi ne ya bayyana haka ranar Alhamis inda yace kungiyar na duba yiyuwar hakan ne saboda ya nayin raunukan da shugaban yaji a jihar Imo ranar Laraba.

A ranar Laraba aka bada rahoton cewa wasu jami’an tsaro sun yi awon gaba da Ajaero a hedikwatar kungiyar ta NLC dake jihar Imo.

Kungiyar ta NLc ta ce an rufe idon Ajaero tare da lakaɗa masa duka bayan da jami’an tsaro suka kama shi.

NLC ta ce an kai shugaban cibiyar kula da lafiya ta tarayya dake Owerri domin samun kulawar likitoci.

Da take musalta kamen hukumar yan sandan jihar ta ce ta ɗauke shugaban kungiyar ta NLC ne domin hana wasu batagarin matasa yi masa duka.

A makon da ya wuce ne kungiyar NLC tayi barazanar tsayar da ayyuka a jihar saboda yadda gwamnan jihar Hope Uzodimma ya gaza biyan ma’aikatan jihar hakkinsu.

More News

Gwamnatin Abia za ta fara biyan albashi mafi maranci na naira 70,000 a watan Oktoba

Gwamnatin Jihar Abia ta sanar da cewa za ta fara biyan sabon albashi mafi karanci na naira 70,000 ga ma’aikatanta daga watan Oktoba 2024.Kwamishinan...

Sojoji sun lalata haramtattun matatun mai 32 a yankin Neja Delta

Dakarun sojan Najeriya na runduna ta 6 dake Fatakwal sun samu nasarar lalata haramtattun matatun man fetur 32 tare da ƙwace lita 250,000 na...

An gudanar da bikin cikar Kwankwaso shekara 68.

Tarin magoya baya da kuma abokanan siyasar tsohon gwamnan jihar Kano, Sanata Rabi'u Kwankwaso ne suka halarci taron lakca da aka shirya domin bikin...

Faruk Lawan ya kammala zaman gidan yarin Kuje

An sako tsohon ɗan majalisar wakilai ta tarayya, Hon Faruk Lawan daga gidan yarin Kuje bayan da ya kammala zaman gidan yarin na shekaru...