Ma’aikatar lafiya ta jihar Lagos ce ta wallafa hakan a shafinta na Twitter a ranar Talata.
Matar mai shekara 30 ta dawo ne daga Birtaniya ranar 13 ga watan Maris – wadda bayan isowarta sai ta killace kanta, inda ta dinga ganin alamun cutar.
Tuni Ma’aikatar Lafiya ta jihar Legas ta yi kira ga duk fasinjojin da suka shigo Najeriya da jirgin British Airways 75, a ranar Juma’a 13 ga watan Maris, da su zauna a gidajensu har tsawon kwana 14.
An yi mata gwaji aka kuma tabbatar ta kamu da Covid-19, inda a halin yanzu take babban Asibitin Gwamnati na jihar da ke Mainland.
Yanzu kasar ta samu mutum uku kenan masu dauke da cutar tun farkon bullarta a Najeriyar ranar 28 ga watan Fabrairun 2020.
Nan gaba a yau ne ake sa ran hukumomin Najeriya za su bayyana wasu matakai kan batun shigowa kasar da kuma shawarwari kan taruwar jama’a.
Dukkan masu cutar uku da aka samu a kasar daga jihar Legas ne.
Matar ita ce mace ta farko da ta kamu a kasar. Coronavirus ta kashe a kalla mutum 7,174 a duniya zuwa yau.
Sannan mutum 182,726 ne suke dauke da Covid-19 a kasashe fiye da 150.