An samu fitowar masu zaɓe da yawa a garin Kankia a zaɓen cike gurbin da ake a Katsina

[ad_1]








An samu fitowar mutane masu yawa a zaben cike gurbin dan majalisar dattawa na mazabar arewacin Katsina da ake gudanarwa yau Asabar.

Fitattun yan takara biyu a zaben, Ahmad Babba Kaita na jam’iyar APC da kuma Alhaji Kabir Babba Kaita na jam’iyar PDP sun fito ne daga gida daya.

Wakilin jaridar Daily Trust ya lura cewa an samu fitowar jama’a masu yawa a tashoshin zabe daban-daban dake garin.

Da yake magana da manema labarai, tsohon dantakarar kujerar gwamnan jihar karkashin jam’iyar PDP a zaben shekarar 2015, Alhaji Musa Nashuni ya yabawa jami’an ƴansanda da kuma hukumar zabe kan yadda ake gudanar da zaben lami lafiya.

“Na ji dadi zaben yana gudana cikin lumana.tabbas wannan zaɓen cike gurbin zai bawa yan Najeriya kyakkyawan fata cewa za a gudanar da zaɓen shekarar 2019 lafiya,” ya ce.




[ad_2]

More News

Mutane uku sun mutu a ruftawar wani ginin bene a Kano

Hukumar Bada Agajin Gaggawa Ta Ƙasa NEMA ta tabbatar da mutuwar mutane uku bayan da wani bene mai hawa uku ya ruguzo a unguwar...

Ganduje Ya Zargi Gwamnatin Kano Da Shirya Zanga-Zangar Neman A Sauke Shi

Shugaban jam'iyar APC na ƙasa, Abdullahi Umar Ganduje ya ce gwamnatin jihar Kano ta jam'iyar NNPP ita ce ke da alhakin shirya zanga-zanga iri...

Qatar za ta taimaki marayu a Najeriya

Gwamnatin kasar Qatar ta bayyana cewa za ta ba da tallafi ga yara marayu sama da 1,000 da suka rasa iyayensu saboda rikicin Boko...

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma’aikatar kudin jihar ta miƙata bayanan bashin da El-Rufai ya ciwo

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma'aikatar kudi ta jihar da ta miƙa mata cikakken bayani kan basukan  da gwamnatin tsohon gwamnan jihar, Nasiru...