An samu bankin Musulunci a karo na biyu a Najeriya

Wani rahoton da muka samu a jiya Litinin daga jaridar Iwitness ta tabbatar da cewa babban bankin Nijeriya, CBN ta bayar da lasisin fara aiki ga wani sabon bankin Musulunci a Nijeriya, mai suna TAJ Bank Limited.

Majiyar mu ta ruwaito babban bankin ta sanar da amincewarta da fara aikin wannan sabon bankin Musuluncin ta cika ne cikin wata wasika data aika mata a ranar Litinin, 15 ga watan Yuli, sakamakon gamsuwa da tayi da cikan dukkan sharuddan data gindaya mata.

Sai dai CBN ta iyakance ayyukan Bankin TAJ a iya yankunan Arewa maso yammaci da kuma Arewa maso gabashin Najeriya, amma ta bata daman ta samar da babban ofishinta a babban birnin tarayya Abuja.

Wannan cigaba da aka samu a harkar cinikayyar kasuwanci irin na Musulunci ya kawo adadin bankunan Musulunci a Najeriya zuwa biyu, bayan samuwar bankin Musulunci na Jaiz tun a shekarar 2011.

Idan za’a tun a shekarar 2003 aka fara haihuwar Jaiz a matsayin cibiyar hada hada cinikayya irin na Musulunci da bata ta’ammali da riba, yayin da a shekarar 2011 CBN ta batalasisin fara aiki a iya Arewacin Najeriya, don haka ta zama bankin Musulunci na farko a Najeriya.

Bankin Musulunci na JAIZ bai fara aiki ba sai a ranar 6 ga watan Janairu na shekarar 2012, inda bayan samun karbuwa suka nemi izinin CBN ta basu daman su fadada ayyukansu zuwa sauran sassan Najeriya, wanda a shekarar 2016 CBN ta bata lasisin aiki a dukkanin sassan Najeriya.

More News

Mutane uku sun mutu a ruftawar wani ginin bene a Kano

Hukumar Bada Agajin Gaggawa Ta Ƙasa NEMA ta tabbatar da mutuwar mutane uku bayan da wani bene mai hawa uku ya ruguzo a unguwar...

Ganduje Ya Zargi Gwamnatin Kano Da Shirya Zanga-Zangar Neman A Sauke Shi

Shugaban jam'iyar APC na ƙasa, Abdullahi Umar Ganduje ya ce gwamnatin jihar Kano ta jam'iyar NNPP ita ce ke da alhakin shirya zanga-zanga iri...

Qatar za ta taimaki marayu a Najeriya

Gwamnatin kasar Qatar ta bayyana cewa za ta ba da tallafi ga yara marayu sama da 1,000 da suka rasa iyayensu saboda rikicin Boko...

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma’aikatar kudin jihar ta miƙata bayanan bashin da El-Rufai ya ciwo

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma'aikatar kudi ta jihar da ta miƙa mata cikakken bayani kan basukan  da gwamnatin tsohon gwamnan jihar, Nasiru...