An rantsar da sabon shugaban kasar DR Congo

Felix Tshisekedi waving after he was announced as winner of the elections in Kinshasa, DR Congo - 10 January 2019

Hakkin mallakar hoto
Reuters

An rantsar da sabon shugaban kasar Jamhuriyar Demokradiyar Congo, Felix Tshiseked a ranar Alhamis.

Ya shaida wa manema labarai a wajen bikin rantsuwar cewa zai hada kan ‘yan Congo.

Mr Tshisekedi ya dan yi fama da gajeriyar rashin lafiya jim kadan kafin ya sha rantsuwar kama mulki.

Daga baya mai magana da yawunsa ya gayawa kamfanin dilancin labarai na Reuters cewa rigar silken da ya sanya ce ta matse shi da yawa.

Ya gaji Joseph Kabila a mika mulki na farko da aka yi cikin lumana cikin shekara 60 da suka gabata, duk da cewa mutane da dama suna tababar samun nasarar tasa.

Sabon shugaban ya yabi tsohon shugaban saboda bar masa mulki da ya yi.

Shugaban kasar Uhuru Kenyatta ne kawai wanda ya halarci bikin rantsuwar cikin shugabannin nahiyar Afirka 17 da aka gayyata.

Hakkin mallakar hoto
Getty Images

An san sabon shugaban a matsayin dan marigayi fitaccen jagoran hamayya Etienne Tshisekedi, wanda ake ganinsa a matsayin daya daga cikin mutane masu muhimmanci da ke rajin kare dimokradiyya na kasar Congo

An kirkiri Jam’iyyar UDPS ta Shugaba Tshisekedi a 1982 kuma mahaifinsa ne ya kirkire ta, wanda ya mayar da ita babbar jam’iyyar adawa.

Amma Shugaba Tshisekedi mai shekara 55, ya yi ta jaddada cewa ba burinsa ya yi adawa da mahaifinsa ba.

More News

Qatar za ta taimaki marayu a Najeriya

Gwamnatin kasar Qatar ta bayyana cewa za ta ba da tallafi ga yara marayu sama da 1,000 da suka rasa iyayensu saboda rikicin Boko...

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma’aikatar kudin jihar ta miĆ™ata bayanan bashin da El-Rufai ya ciwo

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma'aikatar kudi ta jihar da ta miƙa mata cikakken bayani kan basukan  da gwamnatin tsohon gwamnan jihar, Nasiru...

An dakatar da ayyukan kamfanin jiragen sama na Dana Air

Festus Keyamo, ministan harkokin sufurin jiragen sama ya umarci hukumar FAAN dake lura da sufurin jiragen sama a Najeriya ta dakatar da ayyukan kamfanin...

Yahaya Bello Ya Bayyana Dalilan Da Ya Hana Shi Bayyana A Gaban Kotu

Tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello ya ce tsoron kamun  hukumar EFCC dake yaĆ™i da yiwa tattalin arzikin Ć™asa ne ya hana shi bayyana...