An kori jami’an gwamnati kan badakkalar maganin rigakafin jarirai

[ad_1]

Food and Drug Administration officials check on vaccines for rabies at the Disease Control and Prevention Center in Huaibei in China

Hakkin mallakar hoto
Getty Images

An kori wasu manyan jami’an gwamnati masu yawa a sanadiyyar wata matsalar gurbatattun magungunan rigakafi a China da ta ki-ci-ta-ki-cinyewa.

Kimanin jami’ai 40 kuma na fuskantanr matakan ladabtarwa, kuma rahotanni na cewa kamfanin da ake tuhuma ya sayar da nunkin yawan magungunan rigakafi da akan ba jarirai a kasar.

Hukumar da ke kula da ingancin magunguna ta China ta ce kamfanin Changsheng Biotechnology ya sayar da nunkin magungunan rigakafi na ciwon tarin fika da na tetanus.

Magungunan rigakafin da ake magana akai sun zarce 500,000 a halin da ake ciki.

Tuni dai aka kama shugaban kamfanin da wasu mutum 14 a dalilin wannan badakkalar.

Kana wasu jami’an gwamnati da ke da alhakin sa ido kan batutuwan tsaftace abinci da magunguna sun rasa ayyukansu, ciki har da mataimakin gwamnan yankin Jilin na kasar.

Kawo yanzu ba a sami rahotannin cewa wasu jarirai sun sami wani lahani bayan shan wadannan magungunan ba, amma batun ya tayar da hankulan ‘yan kasar game da ingancin magunguna a kasar ta China.

Kafofin watsa labarai mallakin gwamnati sun ruwaito cewa fiye da jami’an gwamnati 40 ne ke fuskantar matakan ladabtarwa a sanadiyyar wannan lamarin.

[ad_2]

More News

Mutane uku sun mutu a ruftawar wani ginin bene a Kano

Hukumar Bada Agajin Gaggawa Ta Ƙasa NEMA ta tabbatar da mutuwar mutane uku bayan da wani bene mai hawa uku ya ruguzo a unguwar...

Ganduje Ya Zargi Gwamnatin Kano Da Shirya Zanga-Zangar Neman A Sauke Shi

Shugaban jam'iyar APC na ƙasa, Abdullahi Umar Ganduje ya ce gwamnatin jihar Kano ta jam'iyar NNPP ita ce ke da alhakin shirya zanga-zanga iri...

Qatar za ta taimaki marayu a Najeriya

Gwamnatin kasar Qatar ta bayyana cewa za ta ba da tallafi ga yara marayu sama da 1,000 da suka rasa iyayensu saboda rikicin Boko...

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma’aikatar kudin jihar ta miÆ™ata bayanan bashin da El-Rufai ya ciwo

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma'aikatar kudi ta jihar da ta miƙa mata cikakken bayani kan basukan  da gwamnatin tsohon gwamnan jihar, Nasiru...