[ad_1]
Barayi dake ɗauke da makamai sun kashe akalla mutane 42 lokacin da suka kaddamar da hare-hare kan wasu ƙauyuka 18 dake lardukan Mashema, Kwashabawa da kuma Birane dake karamar hukumar Zurmi ta jihar a ranar Juma’a.
Wasu majiyoyi sun bayyana cewa adadin mutanen da suka mutu za su iya kai wa 100 domin ba a inda wasu mutanen suka shiga ba.
Jaridar Daily Nigerin ta gano cewa maharan sun kuma kona yawancin gidajen dake ƙauyukan da suka kai harin.
Wani da ya tsira daga harin, Lawali Mashema ya ce dubban mazauna kauyukan da harin ya raba da gidajensu sun gudu zuwa garin Zurmi dake da tazarar kilomita 50 daga garin su.
Wasu da dama kuma na gudun hijira a jihar Katsina da kuma jamhuriyar Nijar.
[ad_2]