An Kashe Mutane 3 A Wani Rikicin Kabilanci A Cross Rives

Mutane 3 ne aka kashe a wani rikicin kabilanci a  Nnaorokpa dake ƙaramar hukumar Nta Ikom ta jihar Cross River.

Mutanen da suka mutu a rikicin sun haɗa  da Rejoice Nton,wata ɗaliba mai shekaru 10, da Mariam Akanya Mfono mai shekaru 20 sai kuma mutum na uku wacce ta kawo ziyara ne yankin.

Mazauna garin sun ce rikici tsakanin Nnaorokpa dake ƙaramar hukumar Nta Ikom da kuma Ofunokpan a ƙaramar hukumar Obubra  ba sabon abu ne domin an ɗauki tsawon shekaru 30 ana yi kuma ya lakume rayukan mutane da dama.

Suka ce rikicin na cigaba faruwa duk da koƙarin da gwamnatin jihar take yi na sasanta rikicin.

Mai magana da yawun rundunar yan sandan jihar,Irene Ugbo ta tabbatar da faruwar lamarin inda ta ce tuni jami’an tsaron suka shawo kan lamarin.

More News

CBN ya dakatar da kudirinsa na sa bankuna su riƙa cajar kwastomominsu

Babban bankin Najeriya ya umarci bankunan da su dakatar da cajin kudaden ajiya har zuwa ranar 30 ga Satumba, 2024.Babban bankin ya bayyana hakan...

Ƴansanda sun kama likitan bogi

Rundunar ‘yan sanda ta Zone 2, Onikan, Legas, ta kama wani likitan jabu mai shekaru 37, kuma ma’aikacin lafiya, tare da zargin amfani da...

Gwamnan Kano ya sanya hannu kan dokar yin gwajin lafiya kafin aure

Gwamnan jihar Kano, Engr Abba Kabir Yusuf ya sanya hannu kan wata doka za ta tilastawa masu yin aure yin wasu gwaje-gwajen lafiya gabanin...

Ƴan sanda sun kama masu garkuwa da mutane da suka yi bacci a lokacin da suke tsare da mutanen da suka sace

Jami'an Æ´an sanda sun samu nasarar kama wasu masu garkuwa da mutane bayan da suka buge da sharar bacci a lokacin da suke tsare...