An kashe masu zanga-zanga a Sudan | BBC Hausa

Juyin Juya halin Sudan

Hakkin mallakar hoto
AFP

Bayanai daga Sudan na cewa an kashe masu zanga-zanga uku da wani jami’in tsaro daya yayin wani artabu a babban birnin Khartoum.

Majalisar soji da ke jagorantar kasar tun bayan hambaras da shugaba Omar Al-Bashir a watan jiya ta ce an jikkata masu zanga-zanga da dama.

Rahotanni sun nuna cewa an samu ci gaba a tattaunawa tsakanin sojoji da wata gamayyar ‘yan adawa wajen kafa hukumar da za ta jagoranci kasar.

  • Yadda zane ke kara rura wutar juyin juya hali a Sudan
  • Sojojin Sudan sun ki amincewa da jagorancin farar hula

Daya daga cikin masu zanga-zangar a Khartoum, babban birnin kasar ta shaidawa BBC cewa “wasu mutane a kayan sojoji” sun harba masu harsashi.

Lina Hieba ta bayyana lamarin a matsayin wani “gagarumin arangama”, inda ta ce an kashe wasu masu zanga-zangar yayin da aka rankaya da wasu asibitoci.

Ta yi watsi da kalaman majalisar soji dake cewa wasu da ba a san ko su waye ba sun harbi masu zanga-zanga, inda ta ce wani yunkuri ne na karkatar da tattaunawar da ake yi tsakanin shugabannin zanga-zangar da sojoji.

“Ba mu yarda da haka ba kuma ba mu amince da su ba,” a cewar Ms Heiba.

A baya dai babban mai shigar da kara na kasar ya ce an tuhumi Mista Bashir da wasu mutane bisa kisan masu zanga-zangar.

More News

Mutane uku sun mutu a ruftawar wani ginin bene a Kano

Hukumar Bada Agajin Gaggawa Ta Ƙasa NEMA ta tabbatar da mutuwar mutane uku bayan da wani bene mai hawa uku ya ruguzo a unguwar...

Ganduje Ya Zargi Gwamnatin Kano Da Shirya Zanga-Zangar Neman A Sauke Shi

Shugaban jam'iyar APC na ƙasa, Abdullahi Umar Ganduje ya ce gwamnatin jihar Kano ta jam'iyar NNPP ita ce ke da alhakin shirya zanga-zanga iri...

Qatar za ta taimaki marayu a Najeriya

Gwamnatin kasar Qatar ta bayyana cewa za ta ba da tallafi ga yara marayu sama da 1,000 da suka rasa iyayensu saboda rikicin Boko...

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma’aikatar kudin jihar ta miƙata bayanan bashin da El-Rufai ya ciwo

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma'aikatar kudi ta jihar da ta miƙa mata cikakken bayani kan basukan  da gwamnatin tsohon gwamnan jihar, Nasiru...