An karrama DPO da yaki karɓar cin hancin $200,000

Babban sifetan yan sanda na kasa, Usman Baba Alkali ya karrama,SP Daniel Itse Ama babbban baturen yan sanda na ƙaramar hukumar Nasarawa dake jihar Kano.

Amah wanda aka rawaito yaki karbar cin hancin kuɗi dalar Amurka 200,000 kan wani laifi da ya shafi fashi da makami.

Laifin na aikata fashi da makami ya shafi wani lauya mai zaman kansa a Kano, da kuma wasu yan sanda guda biyu.

A cikin wata wasikar jinjina, da babban sifetan ya aika masa, ya yabawa Amah kan yadda ya nuna matukar kwarewa da ta kai ga kama, Ali Zaki lauya mai zaman kansa a Kano da kuma wasu yan sanda biyu.

More News

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma’aikatar kudin jihar ta miƙata bayanan bashin da El-Rufai ya ciwo

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma'aikatar kudi ta jihar da ta miƙa mata cikakken bayani kan basukan  da gwamnatin tsohon gwamnan jihar, Nasiru...

An dakatar da ayyukan kamfanin jiragen sama na Dana Air

Festus Keyamo, ministan harkokin sufurin jiragen sama ya umarci hukumar FAAN dake lura da sufurin jiragen sama a Najeriya ta dakatar da ayyukan kamfanin...

Yahaya Bello Ya Bayyana Dalilan Da Ya Hana Shi Bayyana A Gaban Kotu

Tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello ya ce tsoron kamun  hukumar EFCC dake yaƙi da yiwa tattalin arzikin ƙasa ne ya hana shi bayyana...

Ƴan sanda sun kama mutane biyu dake samarwa ƴan fashin daji makamai a jihar Kaduna

Rundunar ƴan sandan jihar Kaduna ta ce tana tsare da wasu mutane biyu da ake zargi da safarar bindiga a jihar. A wata sanarwa ranar...