An Kalubalanci Masu Maganin Gargajiya a Najeriya

VOA Hausa

Gwamnatin Najeriya ta yi kira ga masana kimiyya da masu ruwa da tsaki da su gaggauta yin bincike domin gano maganin cutar coronavirus a cikin gida.

Sakataren gwamnatin tarayya kuma shugaban Kwamitin yaki da cutar ta COVID-19 Boss Mustapha ne ya bayyana hakan a wata hira ta musamman da ya yi da Muryar Amurka.

Kiran na zuwa ne bayan irin alkaluman da ke fitowa daga Hukumar Dakile Yaduwar Cututtuka ta NCDC wadanda ke nuna yadda ake samun hauhawar masu kamuwa da cutar a kullum.

Mustapha ya ce hauhawar adadin mutanen da ke kamuwa da cutar a fadin kasar a kullum ya sa aka fara daukan matakai na tuntubar kwararru da masana musamman ma masu maganin gargajiya na cikin gida.

Ya kara da cewa matakin har ila yau na nuna goyon baya ne da kara kwarin gwiwa domin su fito da basirar su ta kawo magungunan da suke da su saboda a gwada su a kimiyyance.

Sannan a tabbatar da sahihancinsu kafin a yi amfani da su.

Taskar bayanai da ke fitowa daga Hukumar Dakile yaduwar Cututtuka NCDC ta ce a yanzu an samu mutum kusan 6,000 masu dauke da cutar a Najeriya.

Dalilin kenan da ya sa gwamnati ta karbi tayin maganin da kasar Madagascar ta aiko da shi ta hannun Shugaban Guinea Bissau Oumaro Sissoco Embalo.

Amma hukumomin Najeriya sun ce ba za a fara amfani da maganin ba sai kwararru sun tabbatar ba shi da wata illa

Hukumar Lafiya ta Duniya WHO ta yi kira da a yi gwajen-gwajen magungunan da ake samu kafin a fara amfani da su

More News

Zanga-zanga: An jibge Æ´an sanda 4200 a Abuja

Rundunar Æ´an sandan birnin tarayya Abuja ta tura Æ´an sanda 4200 gabanin zanga-zangar da za a gudanar a cikin watan Agusta. Kamar yadda masu shirya...

Kamfanin NNPC ya shirya daukar karin ma’aikata

Kamfanin mai na Nigerian National Petroleum Company Limited ya shirya daukar karin ma’aikata.Kakakin kamfanin na NNPC, Olufemi Soneye, ya tabbatar da hakan a wata...

Ya kamata matasa su yi haÆ™uri zanga-zanga ba ita ce mafita ba – Sarkin Zazzau

Sarkin Zazzau, Mai Martaba Ahmed Nuhu Bamalli ya ce matasa su ƙara haƙuri da gwamnatin tarayya su janye zanga-zangar da suka shirya gudanarwa a...

Zanga-zanga: Tinubu ya gana da gwamnonin APC

Shugaban ƙasa, Bola Ahmad Tinubu ya gana da gwamnonin da aka zaɓa ƙarƙashin jam'iyar APC. Taron ganawar da aka gudanar a fadar shugaban ƙasa ta...