An tura dakarun sojin saman Najeriya da jirgin yaki da makamai zuwa Sokoto domin yaki da ‘yan fashi da masu garkuwa mutane.
Sanarwa da kakakin rundunar sojin sama Ibikunle Daramola ya tura wa manema labarai, ta ce an tura dakarun ne tare da jirgin yaki domin taimakawa rundunar Operation Diran Mikiya da ke yaki da ‘yan bindiga tsakanin kan iyakar Sokoto da Zamfara da Katsina
Tuni sojojin suka isa Sokoto a ranar Lahadi domin soma yaki da ‘yan fashi da suka addabi yankin na arewa maso yammacin Najeriya.
- An kama ‘yan bindigar da suka sace tagwaye a Zamfara
- ‘Yan sa-kai na ‘kashe mutane a kasuwannin Zamfara’
Babban kwamandan sojin sama a Sokoto Air Vice Marshal Oladayo Amao da ya tarbi sojojin, ya bukaci su nuna kwarewa ga aikin da aka turo su na tabbatar da tsaron al’umma da kuma yakar ‘yan fashi.
Sanarwar ta kuma ce za a inganta filin jirgin Sultan Abubakar III a Sokoto da dukkanin abubuwan da suka wajaba domin kaddamar da hari ta sama daga tashar jirgin saman.
[ad_2]