Hukumomi a arewacin Burkina Faso sun ce an kashe mutane akalla 29 a wasu hare-hare daban guda biyu da ake zargin Musulmi masu ikirarin Jihadi ne suka kai.
A wata sanarwa, gwamnatin Burkina Fason ta ce mutane akalla 15 ne suka mutu, shida kuma suka samu raunuka, lokacin da wata babbar mota ta taka wata nakiya ko bam a lardin Sanmatenga.
Sannan kuma a wani hari da aka kai kan jerin gwanon wasu motoci da ke dauke da kayan abinci da za a kai wa ‘yan gudun hijira, an kashe farar hula akalla goma in ji hukumomi.
Gwamnatin Burkina Fason ta ce tuni an tura karin sojoji yankin domin kai dauki.
Kasar dai ta fara fama da hare-haren masu ikirarin Jihadi, da suka bazu zuwa can daga Mali, zuwa Arewaci, sannan kuma zuwa gabashin Burkina Fason a 2015.
Tun daga sannan da abin ya fara an yi kiyashin hallaka mutane sama da 500 a kasar ta yammacin Afirka.
Daga nan kasar ta Burkina Faso ta kasance daga kasashen katafaren yankin Sahel da ke fama da tashin hankali na kungiyoyin Musulmi masu ikirarrin Jihadi a yankin.
Ita tare da makwabtanta na yankin Nijar, Chadi, da Mauritania da kuma Mali suka hadu suka samar da dakarun kungiyar da ake kira, G5 Sahel, domin kawar da barazanar mayakan.
A watan Janairu Firaministan kasar, PM Paul Kaba Thieba ya sauka daga aiki sakamakon matsin-lamba a kan karin sace-sacen jama’a da hare-haren masu ikirarin Jihadin, aka kuma maye gurbinsa da Christophe Joseph Marie Dabiré.
Tsohuwar uwar-gijiyar yankin ta mulkin mallaka, wato Faransa, tana da dakaru 4,500 a kasashe hudu, domin yakar masu tayar da kayar bayan Musulmi.