An halaka mutane 6 a wani faɗa tsakanin ƴanbindiga da ƴanbanga

Mutane 6 ne suka rasa rayukansu a wata arangama da aka yi tsakanin ‘yan bindiga da ’yan banga da aka fi sani da ‘Yan Sakai a karamar hukumar Gada a jihar Sakkwato.

‘Yan bangar, a cewar wata majiya a yankin da ta nemi a sakaya sunanta saboda yadda lamarin ya kasance, an ce sun dauki fansa ne kan kisan da wasu ‘yan bindiga suka yi wa shugabansu, Alhaji Dahiru.

Shaidun gani-da-ido sun ce rikicin ya fara ne a lokacin da wani jagoran ‘yan banga kauyen Gidan Hashimu ya yi wani yunkuri na kama wasu barayin shanu.

Rahotanni sun ce ‘yan bindigar da ake zargin, a daidai lokacin da rikicin ya yi kamari, sun harbe shugaban ‘yan bangan har lahira, lamarin da ya janyo ramuwar gayya daga ‘yan banga.

Daya daga cikin shaidun gani da ido ya ce kafin isowar tawagar jami’an tsaron kasuwar, sama da mutum shida ne suka mutu.

More News

Mai magana da yawun Tinubu ya ajiye aikinsa na wani lokaci

Mai ba shugaban kasa shawara na musamman kan harkokin yada labarai Ajuri Ngelale ya ajiye aikinsa na wani lokaci domin tunkarar matsalar lafiya.Mista Ngelale...

Ali Jita ya koma jam’iyar APC daga NNPP

Mataimakin shugaban majalisar dattawa dattawa, Sanata Barau Jibrin ya karɓi fitaccen mawakin Kannywood, Aliyu Isa Jita daga jam'iyar NNPP ya zuwa jam'iyar APC. Ali Jita...

An yi jana’izar mutumin da ya ƙirƙiri tutar Najeriya

Iyalan marigayi, Pa Taiwo Akinkumi mutumin da ya ƙirƙiro tutar Najeriya sun yi bikin binne shi bayan da gwamnatin tarayya ta gaza cika alƙawarin...

‘Za a ƙara wa ƴan bautar ƙasa na NYSC alawus’

Babban daraktan hukumar yi wa kasa hidima ta kasa (NYSC) Birgediya Janar Yushau Ahmed, ya tabbatar wa ‘yan bautar kasar cewa za a kara...