An dawo da zirga-zirgar jiragen sama a filin jirgin saman Kaduna

Bayan dakatarwar watanni 19 saboda dalilan tsaro dake da alaka da yan bindiga zirga-zirgar jiragen saman Hassan Usman Katsina dake Kaduna.

Saukar jirgin saman kamfanin Air Peace kirar ERJ-145 wanda ya sauka a filin jirgin da karfe 05:10 na yamma shi yake nuna dawowar cigaba da zirga-zirgar jiragen sama a filin jirgin.

Idan za a iya tunawa a cikin watan Maris na shekarar 2022 a ka samu hare-haren yan bindiga a yankin dake kusa da filin jirgin har ya jawo an dakatar da zirga-zirga ta wucin gadi kafin daga baya jirgin kamfanin Azman ya dawo cigaba da zirga-zirga a filin jirgin.

Hakan ya tilastawa fasinjoji masu zuwa Kaduna daga Lagos su sauka a Abuja ko Kano sannan su hau mota zuwa Kaduna.

Manajan filin jirgin, Adamu Sheikh wanda ya bayyana cewa kamfanonin jiragen sama da dama na shirye-shiryen sake fara fara zirga-zirga a filin jirgin inda ya jaddada aiwatar da tsauraran matakan tsaro domin sauka da kuma tashin jiragen sama.

More News

CBN ya dakatar da kudirinsa na sa bankuna su riƙa cajar kwastomominsu

Babban bankin Najeriya ya umarci bankunan da su dakatar da cajin kudaden ajiya har zuwa ranar 30 ga Satumba, 2024.Babban bankin ya bayyana hakan...

Ƴansanda sun kama likitan bogi

Rundunar ‘yan sanda ta Zone 2, Onikan, Legas, ta kama wani likitan jabu mai shekaru 37, kuma ma’aikacin lafiya, tare da zargin amfani da...

Gwamnan Kano ya sanya hannu kan dokar yin gwajin lafiya kafin aure

Gwamnan jihar Kano, Engr Abba Kabir Yusuf ya sanya hannu kan wata doka za ta tilastawa masu yin aure yin wasu gwaje-gwajen lafiya gabanin...

Ƴan sanda sun kama masu garkuwa da mutane da suka yi bacci a lokacin da suke tsare da mutanen da suka sace

Jami'an Æ´an sanda sun samu nasarar kama wasu masu garkuwa da mutane bayan da suka buge da sharar bacci a lokacin da suke tsare...