Ƴan Najeriya da basu gaza 108 da aka dawo su daga Libiya gwamnatin tarayya ta karɓa ta hannun hukumar Bada Agajin Gaggawa Ta Ƙasa NEMA.
Waɗanda aka dawo dasu an ɗauko daga birnin Tripoli cikin jirgin kamfanin Al Buraq Air kirar Boeing 737-800 ya sauka a bangaren jirgin kaya na filin jirgin saman Murtala Muhammad dake Lagos da misalin karfe 05:55 na yamma.
Masu dowawar wanda kungiyar IMO ta majalisar dinkin duniya dake lura da yan gudun hijira ta taimaka musu wajen dawowa sun haɗa manyan mata 46 kananan yaran mata biyu da kuma jaririya ɗaya.
Sauran sun haɗa da maza manya 52 kananan yara 4 da kuma jarirai maza 4.
Da yake karɓar mutanen shugaban hukumar ta NEMA, Mustapha Habib Ahmed ya sake jaddada aniyar sabuwar gwamnatin Bola Ahmad Tinubu na magance kalubalen da matasa ke fuskanta.