An dakatar da dokar hana fita a Kano

Rundunar ‘yan sanda a jihar Kano ta bayar da sanarwar kawo karshen dokar hana fita ta tsawon sa’a 24, da aka sanya a jihar.

Mai magana da yawun rundunar, SP Abdulahi Haruna Kiyawa ne ya sanar da haka a wani sako da ya wallafa a shafin Facebook.

A ranar Laraba ne dai rundunar ƴan sandan Kano ta sanya dokar bayan yanke hukuncin kotun sauraron ƙorafe-ƙorafen zaɓen gwamna, da ya soke nasarar Abba Kabir Yusuf, tare da ayyana Nasiru Yusuf Gawuna a matsayin halastaccen gwamna.

More from this stream

Recomended

Kotun Tarayya Ta Tabbatar Da David Mark A Matsayin Shugaban ADC

Wata babbar kotun tarayya da ke Abuja ta tabbatar da shugabancin jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) ƙarƙashin jagorancin tsohon shugaban majalisar dattawa, David Mark. Kotun ta yi watsi da ƙarar da ɗan majalisar wakilai, Leke Abejide, ya shigar kan shugabancin jam’iyyar, inda ta bayyana cewa lamarin ya shafi harkokin cikin gida na jam’iyyar siyasa. Mai […]