An dage shari’ar Babachir Lawal

Babachir a kotu

Image caption

Babachir a kotu

Wata kotu da ke zamanta a Abuja, birnin tarayyar Najeriya, ta dage shari’ar tsohon sakataren gwamnatin tarayya a kasar Babacir Lawal zuwa ranar Laraba.

Kotun dai ta bayar da umarnin cewa hukumar EFCC ta ci gaba da tsare Mista Lawal.

A lokacin sauraren karar, lauyan Mista Lawal ya bukaci da a bai wa wanda yake karewa beli.

Amma lauyoyin EFCC da suka shigar da karar Babachir suka nemi kotu ta yi watsi da bukatar bayar da belinsa.

EFCC na zargin tsohon sakataren gwamnatin ne da laifin karkatar da kudaden da aka ware wa ‘yan gudun hijira da rikicin Boko Haram ya daidaita.

Wannan zargin ne ya sa shugaba Muhammadu Buhari ya kore shi daga gwamnatinsa.

Tun bayan sauke Babachir daga mukaminsa, ‘yan Najeriya ke ta ce-ce-ku-ce musamman kan tafiyar hawainiya da gwamnatin Buhari ke yi wajen gurfanar da Mista Lawal a gaban kotu.

Wannan shari’ar na zuwa ne kasa da mako daya a gudanar da babban zabe a kasar.

More News

Mutane uku sun mutu a ruftawar wani ginin bene a Kano

Hukumar Bada Agajin Gaggawa Ta Ƙasa NEMA ta tabbatar da mutuwar mutane uku bayan da wani bene mai hawa uku ya ruguzo a unguwar...

Ganduje Ya Zargi Gwamnatin Kano Da Shirya Zanga-Zangar Neman A Sauke Shi

Shugaban jam'iyar APC na ƙasa, Abdullahi Umar Ganduje ya ce gwamnatin jihar Kano ta jam'iyar NNPP ita ce ke da alhakin shirya zanga-zanga iri...

Qatar za ta taimaki marayu a Najeriya

Gwamnatin kasar Qatar ta bayyana cewa za ta ba da tallafi ga yara marayu sama da 1,000 da suka rasa iyayensu saboda rikicin Boko...

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma’aikatar kudin jihar ta miƙata bayanan bashin da El-Rufai ya ciwo

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma'aikatar kudi ta jihar da ta miƙa mata cikakken bayani kan basukan  da gwamnatin tsohon gwamnan jihar, Nasiru...