An ɗage sauraron shari’ar Hadizan Gabon

Khadi Rilawanu Kyaudai na kotun shari’ar musulunci dake zamanta a Magajin Gari Zariya,ya dage shari’ar da yake sauraro tsakanin yar wasan Kannywood, Hadiza Gabon da Kuma Wani ma’aikacin gwamnati mai suna Bala Musa.

Ana tuhumar Gabon da laifin zanbatar Bala bayan da ta karɓe masa yan kudade da sunan zata aure shi.

An dage zaman shari’ar zuwa ranar, 1 ga watan Agusta biyo bayan yanayin rashin lafiya da matar alkalin take ciki.

Musa ya kai karar ne inda yake bukatar jaruma Gabon ta dawo masa da kudinsa,396,000 bayan da taki amincewa ta aure shi.

Tuni dai jarumar ta musalta cewa akwai wannan alƙawari a yayin zaman kotun da aka yi na farko a ranar 14 ga watan Yuni.

Jaridar Daily Trust ta rawaito cewa bayan da kowa ya gama hallara domin fara sauraren shari’ar na ranar Talata sai alkalin ya sanar cewa ya samun labarin an kai ɗaya daga cikin matansa a asibiti.

More News

Mutane uku sun mutu a ruftawar wani ginin bene a Kano

Hukumar Bada Agajin Gaggawa Ta Ƙasa NEMA ta tabbatar da mutuwar mutane uku bayan da wani bene mai hawa uku ya ruguzo a unguwar...

Ganduje Ya Zargi Gwamnatin Kano Da Shirya Zanga-Zangar Neman A Sauke Shi

Shugaban jam'iyar APC na ƙasa, Abdullahi Umar Ganduje ya ce gwamnatin jihar Kano ta jam'iyar NNPP ita ce ke da alhakin shirya zanga-zanga iri...

An kashe kwamandan soji a Katsina

An kashe kwamandan sojoji na wani sansanin soji da ke Sabon Garin Dan’Ali a karamar hukumar Danmusa a jihar Katsina a wani harin kwantan...

Qatar za ta taimaki marayu a Najeriya

Gwamnatin kasar Qatar ta bayyana cewa za ta ba da tallafi ga yara marayu sama da 1,000 da suka rasa iyayensu saboda rikicin Boko...