Birtaniya da Amurka sun gaya wa kwamitin tsaro na Majalisar Dinkin Duniya cewa gwamnatocin kasashen Sahel da ke Afirka ta Yamma ba sa yin abin da ya kamata domin kawo karshen tashin hankalin da ke addabar yankin.
Duk da kasancewar dubban dakarun yankin da na wasu kasashe a Mali da Nijar da kuma Burkina Faso, ana samun karuwar hare-haren kungiyoyin masu tayar da kayar baya da ke da alaka da Al Qaeda da kuma IS.
Bisa ga dukkan alamu baki kusan ya zo daya cewa abubuwan da ke haddasa ko kuma suka haddasa hare-hare da tashin hankalin masu tayar da kayar baya da ke da nasaba da addini a yankin na Sahel, a kwai rashin jituwa da zaman doya da manja tsakanin saboda filayen kiwo ko noma da ruwa, wanda akwai bukatar show kan wannan matsala.
Da yake jawabi ga ‘yan kwamitin tsaro na majalisar Dinkin Duniya, mataimakin jakadan Amurka a Majalisar, ya ce matakin soji kadai da ake dauka a yankin ba zai raba alumma da tashe-tashen hankali ba.
Ya ce akwai bukatar samun yanayi na juriya da hakurin zama tare da samun gwamnatoci na gari da kuma wanzuwar kungiyoyin kare hakkin jama’a masu karsashi, kafin a samu zaman lafiya da ci gaba a yankin.
Shi ma jakadan Birtaniya a Majalisar ta Dinkin Duniya ya kara ne da cewa, dole ne a magance matsalar cin hanci da rashawa da rashin ayyuka da karancin ababan bunkasa rayuwar jama’a da kawar da matsalar rashin dama ga matasa, kafin yankin na Sahel ya fito daga kangin tashin hankali na masu tayar da kayar-baya da koma-baya da yake ciki.
Sai dai kuma duk da wannan a yanzu shugabannin kasashen yankin na neman karin taimako na soji, ganin yadda daruruwan sojojinsu ke fadi-tashin rike iko a inda suke gwagwarmaya da masu tayar da kayar baya.
Ana sa ran a watan Janairu Faransa da ke da dakaru 4500 a fadin yankin na Sahel za ta yi taron koli na tsaro domin tattauna batun kasancewar sojin nata a yankin.
An ruwaito hafsan hafsoshin Faransar Janar Francois Locontre, yana bayyana cewa makomar yankin na Sahel za ta danganta ne da abin da zai faru a shekara mai zuwa.
Ya bayyana cewa idan aka bari rikicin da ake fama da shi a yanzu ya dabaibaye yankin, ‘yan kungiyar IS za su mamaye shi.
Ya bayyana cewa matakan da sojoji ke dauka kadai ba za su karya ‘yan kungiyar ba, da kuma kawo karshen wasu rikice-rikice a yankin na Sahel, sai an kawo wata mafita ta hanyar siyasa.
Janar Francois ya kare dakarun Faransar da ke yakar masu ikirarin jihadi a yankin na Sahel. inda ya ce Faransa za ta kai wannan yaki mataki na gaba.