Amurka ba ta da kwarewa, inji Taliban

Hibatullah Akhundzada shi ne sabon shugaban Taliban a Afghanistan

Image caption

Hibatullah Akhundzada, tsohon shugaban kotunan Taliban, shi ne sabon shugaban kungiyar a Afghanistan,

Kungiyar Taliban ta mayar da martani kan matakin Shugaba Trump na yin watsi da yarjejeniyar zaman lafiya a Afghanistan, tare da fasa ganawar sirri da ya shirya yi da shugabannin kungiyar a Amurka.

Shugaban ya dauki matakin ne bayan wani wawan hari da kungiyar ta kai ranar Alhamis wanda ya hallaka mutane 12 ciki har da sojan Amurka daya.

Hakkin mallakar hoto
Getty Images

Image caption

Taliban ta kai hare-hare da dama a Afghanistan ciki har da na majalisar dokokin kasar a watan Yuni na 2015

A martanin kungiyar ta ce matakin shugaban ya nuna rashin kwarewa da kuma aniyar Amurka kan rikicin na Afghanistan;

A martanin nata kungiyar Taliban ta ce komai na tafiya lami lafiya kafin Shugaba Trump ya soke ganawarsu.

A sanarwar da kungyar ta fitar ta ce, an gayyaci shugabanninta zuwa Amurka a karshen watan Agusta, amma suka jinkirta har sai an kammala sanya hannu a yarjejeniyar da ake yi. Haka su ma kasashen yankin sun mara baya ga hakan.

Kungiyar ta ce tun da yanzu shugaban Amurkar ya soke tattaunawar zaman lafiyar, Amurka ce za ta fi yin asara, za ta rasa kimarta, sannan a yanzu za a kara sanin matsayi da manufarta kan batun zaman lafiya, wato za a san cewa ba da gaske take ba.

Image caption

Akwai kungiyoyin mayaka daban-daban na Taliban

A sanarwar Taliban ta ce, a bangarensu, sun tabbatar cewa, yaki dai kai musu shi aka yi, kuma a duk lokacin da ake da niyyar tattaunawa, a shirye suke.

Ta ce ficewa daga tattaunawar zaman lafiya kafin sanya hannu a yarjejeniyar, saboda hari ko fashewa daya kawai, hakan ya nuna rashin hakuri ko kwarewar Amurka, musamman ma a lokacin da rayuka da dukiyar tarin ‘yan Afghanistan suka salwanta a sanadiyyar hare-haren Amurka da kawayenta a Afghanistan.

Taliban din ta ce, tana da kwakkwarar manufa da zaman lafiya, domin shekara ashirin baya ta ce ta nemi a zauna a tattauna, kuma har a yau din nan a shirye take da hakan.

A karshe sun ce sun yi amanna, nan ba da jimawa ba Amurkawan ma za su cimma wannan matsaya.

Matakin na Shugaba Trump ya kasance tamkar wata babbar mahangurba ga shirin wanzar da zaman lafiyar a Afghanistan, matakin da harin da ‘yan Taliban suka kai wanda ya harzuka shugaban kasancewar akwai sojan Amurka daya tilo daga cikin mutum 12 da harin na Kabul ya hallaka a ranar Alhamis.

Tattaunawar yarjejeniyar dai na wakana lafiya kalau, da har da dama daga jama’ar Afghanistan na murna da ganin ana dab da kawo karshen rikicin da kusan a kullum ke musu taannati na rayuka da dukiya da zaman lafiya shekara da shekaru.

More News

Qatar za ta taimaki marayu a Najeriya

Gwamnatin kasar Qatar ta bayyana cewa za ta ba da tallafi ga yara marayu sama da 1,000 da suka rasa iyayensu saboda rikicin Boko...

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma’aikatar kudin jihar ta miĆ™ata bayanan bashin da El-Rufai ya ciwo

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma'aikatar kudi ta jihar da ta miƙa mata cikakken bayani kan basukan  da gwamnatin tsohon gwamnan jihar, Nasiru...

An dakatar da ayyukan kamfanin jiragen sama na Dana Air

Festus Keyamo, ministan harkokin sufurin jiragen sama ya umarci hukumar FAAN dake lura da sufurin jiragen sama a Najeriya ta dakatar da ayyukan kamfanin...

Yahaya Bello Ya Bayyana Dalilan Da Ya Hana Shi Bayyana A Gaban Kotu

Tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello ya ce tsoron kamun  hukumar EFCC dake yaĆ™i da yiwa tattalin arzikin Ć™asa ne ya hana shi bayyana...