Amokachi ya taya Mansurah da Sani Danja murnar shekara 12 da yin aure

Mansurah da Sani Danja

Hakkin mallakar hoto
@mansurah_isah

Tsohon dan wasan Super Eagles na Najeriya Daniel Amokachi ya taya jaruman Kannywood Mansurah Isah da mijinta Sani Danja murnar cika shekara 12 da aurensu.

Sani Danja da Mansurah suna cikin ‘yan fim na farko-farko da suka auren juna, kuma sakon da suka wallafa a shafin Instagram ya ja hankalin jama’a sosai ciki har da tsohon dan kwallon na Najeriya.

A cikin sakon da tsohuwar jarumar fina-finan na Hausa ta wallafa mai dauke da hoton mijinta, ta yi takaitaccen bayani game da rayuwar aurensu na zaman hakuri da kaunar juna.

Kalaman sun nuna yadda kamar a gidaje da dama, ma’auratan ke zaman hakuri duk da irin sabanin da ta ce suna samu a lokaci zuwa lokaci.

Wannan na zuwa ne a daidai lokacin da ake yawan samun rahotanni marasa dadin ji na yawaitar mutuwar aure a arewacin Najeriya da kuma kisa ko kaiwa juna hari tsakanin wasu ma’auratan, lamarin da ake alakantawa da rashin soyayya, hakuri da rashin bin tsari mai kyau wurin assasa auren.

Mansurah ta ce dukkaninsu suna da rauni, inda wani lokaci takan yi gaba da mijinta ba tare da ya saba mata ba, yayin da wani lokaci kuma ya ki cin abincinta har ya ki ba ta kudi idan ta tambaye shi.

“Ka ci gaba da hakuri da ni ka ci gaba da dauke kai a kan laififfuka na. Domin nasan ni mai laifi ce a gare ka. Rayuwa ba ka taba zama 100% komin yaya akwai inda ka kasa,” in ji ta.

Amma ta ce sukan yi dariyar sabanin da suke samu saboda sun zama abokan juna. Kuma har yanzu suna son junansu kuma suna taimakon juna.

Hakkin mallakar hoto
Michelly Rall

Image caption

Daniel Amokachi ya shahara wurin taka kwallo a ciki da wajen Najeriya

Ta kuma yaba wa yadda ta ce mijin nata ya yi hakurin zama da kuma kula da ita.

Kalaman sun sa mutane da dama yi mata da mijinta fatan alheri da dorewar zaman lafiya a aurensu, kuma cikinsu har da Daniel Amokachi.

Amokachi ya yi masu addu’a inda ya ce Allah Ya ci gaba da ba su zaman lafiya da kara kauna, bayan ya taya su murna.

Hakkin mallakar hoto
Awwal Ahmad

Wata daga cikin wadanda suka yi tsokaci ta ce, kalaman Mansurah sun kusan sa ta yin kwalla. Inda ta yi addu’a cewa Allah Ya kara daidaita tsakaninsu.

Mabiya sama da 800 ne suka yi tsokaci, yayin da kusan mabiya 15,000 suka so sakon.

More News

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma’aikatar kudin jihar ta miÆ™ata bayanan bashin da El-Rufai ya ciwo

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma'aikatar kudi ta jihar da ta miƙa mata cikakken bayani kan basukan  da gwamnatin tsohon gwamnan jihar, Nasiru...

An dakatar da ayyukan kamfanin jiragen sama na Dana Air

Festus Keyamo, ministan harkokin sufurin jiragen sama ya umarci hukumar FAAN dake lura da sufurin jiragen sama a Najeriya ta dakatar da ayyukan kamfanin...

Yahaya Bello Ya Bayyana Dalilan Da Ya Hana Shi Bayyana A Gaban Kotu

Tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello ya ce tsoron kamun  hukumar EFCC dake yaÆ™i da yiwa tattalin arzikin Æ™asa ne ya hana shi bayyana...

Ƴan sanda sun kama mutane biyu dake samarwa ƴan fashin daji makamai a jihar Kaduna

Rundunar Æ´an sandan jihar Kaduna ta ce tana tsare da wasu mutane biyu da ake zargi da safarar bindiga a jihar. A wata sanarwa ranar...