Ambaliyar ruwa ta yi sanadin mutuwar mayaƙan Boko Haram ‘sama da 100’

Asalin hoton, Nig Army

Gwamman mayaƙa masu iƙirarin jihadi na Ƙungiyar Boko Haram sun mutu a ruwa yayin da suke guduwa daga hari ta sama da ƙasa da sojojin Najeriya ke yi musu a Jihar Borno.

Jami’an tsaron ƙasar sun ce sun kai hari ne a maɓoyar mayaƙan a can cikin dajin Sambisa.

Rahotanni sun ce baya ga farmakin sojojin, akwai ɗaruruwan mayaƙan da suka tsere tare da iyalansu sakamakon ambaliyar ruwa da ta mamaye sansanoninsu.

Mayaƙan sa kai waɗanda ke yaƙar ƴan Boko Haram din sun bayyana cewa sun zaƙulo gawarwaki sama da 100 daga cikin kogi inda suka binne su.

Karin wasu labaran da za ku so ku karanta

Rahotanni sun ce ambaliyar da Kogin Yedzaram ya yi ne ya jawo ambaliyar da ta shafi sansanonin mayaƙan da dama, lamarin da ya ja suka yi hijira.

Dubban mutane ne dai suka mutu, kuma kusan mutum miliyan biyu ne mayaƙan na Boko Haram suka raba da muhallansu.

Sai dai a ƴan kwanakin nan jami’an tsaron ƙasar sun ce ana samun sauƙi sakamakon irn farmakin da suke kai wa mayaƙan.

Haka kuma ana samun wasu daga cikin mayaƙan na Boko Haram da suke tuba suna miƙa wuta.

Kazalika wasu kuma sun bazama inda suke haɗewa da wasu ƙungiyoyi masu iƙirarin jihadin irin su ISWAP da ta fi ƙarfi a arewa maso gabas da kuma ANSARU da ke da ƙarfi a arewa maso takiya da kuma wani fanni na arewa maso yammacin Najeriya.

More News

Mai magana da yawun Tinubu ya ajiye aikinsa na wani lokaci

Mai ba shugaban kasa shawara na musamman kan harkokin yada labarai Ajuri Ngelale ya ajiye aikinsa na wani lokaci domin tunkarar matsalar lafiya.Mista Ngelale...

Ali Jita ya koma jam’iyar APC daga NNPP

Mataimakin shugaban majalisar dattawa dattawa, Sanata Barau Jibrin ya karɓi fitaccen mawakin Kannywood, Aliyu Isa Jita daga jam'iyar NNPP ya zuwa jam'iyar APC. Ali Jita...

An yi jana’izar mutumin da ya ƙirƙiri tutar Najeriya

Iyalan marigayi, Pa Taiwo Akinkumi mutumin da ya ƙirƙiro tutar Najeriya sun yi bikin binne shi bayan da gwamnatin tarayya ta gaza cika alƙawarin...

‘Za a ƙara wa ƴan bautar ƙasa na NYSC alawus’

Babban daraktan hukumar yi wa kasa hidima ta kasa (NYSC) Birgediya Janar Yushau Ahmed, ya tabbatar wa ‘yan bautar kasar cewa za a kara...