Al’umman Kaduna Na Korafin Karuwar Aikin Yan Bindiga a Jihar – AREWA News


A hirar shi da Muryar Amurka, daya daga cikin al’umar yankin, Malam Yusuf Ibrahim Udawa ya ce baya ga hare-haren yan-bindiga, su kan kuma shiga su karbi kudaden al’uma sannan su yi lalata da matan mutane.
Wannan korafi dai na zuwa ne kwanaki biyu da fitar da rahoton tsaro da gwamnatin jahar Kaduna ta yi inda ta bayyana nasarorin da ta ke samu kan maharan dajin baki daya.
Kaduna dai na cikin jihohin Arewan maso yammacin da ke fama da hare-haren ‘yan-bindiga masamman dai satar dalibai wadda har yanzu akwai daliban makarantun da ba a dawo da su ba.
(VOA Hausa)

More News

An kashe kwamandan soji a Katsina

An kashe kwamandan sojoji na wani sansanin soji da ke Sabon Garin Dan’Ali a karamar hukumar Danmusa a jihar Katsina a wani harin kwantan...

Magoya bayan APC da dama sun koma NNPP a Kano

Jam'iyar NNPP ta karɓi magoya bayan jam'iyar APC da dama a jihar Kano. Mataimakin gwamnan jihar Kano, Aminu Abdul Salam Gwarzo shi ne ya karɓi...

APC ta dakatar da Ganduje a matakin gunduma

Mambobin jam'iyyar APC a mazabar da ke Karamar Hukumar Dawakin Tofa a Jihar Kano sun dakatar da Shugaban Jam’iyyar APC na kasa Abdullahi Ganduje. ...

Yadda rikici a kan gishirin N20 ya yi sanadiyyar mutuwar wani mutum a Kano

Wani magidanci mai suna Zakari Hamza mai shekaru 45, ya gamu da ajalinsa a hannun kanen matarsa, wani Magaji Salisu saboda gishirin N20. Dan marigayin,...