Aliko Dangote da Bill Gates sun gana da shugaba Tinubu a Abuja

Bill Gates, wanda ya kafa Microsoft, da Aliko Dangote, shugaban rukunin Dangote, sun gana da shugaba Bola Tinubu a ranar Litinin a fadar shugaban kasa da ke Abuja.

Dayo Olusegun, mai taimaka wa Tinubu kan harkokin yada labarai ne ya wallafa a shafinsa na Twitter game da taron.

A cewar Olusegun: “Mr @BillGates, shugaban gidauniyar Bill and Melinda Gates kuma wanda ya kafa Microsoft ya isa fadar shugaban kasa a Villa tare da Alhaji @ Aliko Dangote domin ganin shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu (GCFR).”

Ku tuna cewa Dangote ya bayyana a makon jiya cewa Tinubu da Gates za su yi taro a yau.

More News

Ƴan sanda sun kama mutane 50 kan rikicin da ya faru a wata kasuwa a Lagos

Rundunar Æ´an sandan jihar Legas ta kama mutane sama da 50 da ake zargin suna da hannu rikicin da ya faru a kasuwar Ile...

Ƴan Sanda sun kama wanda ya shirya kai harin jirgin ƙasar Abuja-Kaduna a shekarar 2022

Rundunar ƴan sandan Najeriya ta ce jami'anta sun kama wani mutum mai suna Ibrahim Abdullahi wanda ake zargi da kitsa harin jirgin ƙasar da...

Ƴansanda sun kama wanda ya kitsa harin da aka kai wa jirgin ƙasa a Kaduna

Rundunar ‘yan sandan Najeriya a ranar Alhamis, ta sanar da kame wanda ake zargin ya shirya harin da aka kai a jirgin ƙasan Abuja-Kaduna...

Sojoji Sun Ceto Mutane Daga Hannun Masu Garkuwa Da Mutane A Filato

Dakarun rundunar Operation Safe Haven dake aikin tabbatar da tsaro a jihar Filato da wani É“angare na jihar Kaduna sun samu nasarar ceto mutane...