Aisha Buhari Ta Gargadi Iyaye Su Hana ‘Ya’yansu Fada A Ranar Zabe

Madam Dolakpo Osinbajo ta bayyana hakan ne a wurin gangamin yakin neman zaben jami’iyyar APC da aka shiryawa mata da matasa a shiyyar jihohin tsakiyar Najeriya da aka gudanar a garin Lafia, babban birnin jahar Nasarawa.

Uwargidan mataimakin shugaban kasar wacce ta wakilci matar shugaban kasa, Hajiya A’isha Buhari ta zayyana ayyukan ci gaba da shugaba Muhammadu Buhari ya yiwa yara da mata da suka hada da shirin ciyar da ‘yan makarantar firamare kyauta wanda ya baiwa mata ayyukan yi, da tallafin kudi wa kananan ‘yan kasuwa da ake wa lakabi da Trader Moni da bayyana tabbacin kowa zai fita daga kangin talauci.

Da take magana da yawun uwargidan shugaban kasar A’isha Buhari, Dolakpo Osinbajo tace kada iyaye su kyale ‘ya’yansu su yi fada a lokacin zabe, sai dais u kada kuri’arsu su je gida su jira sakamakon zabe.

Ministan inganta wasanni da matasa yana cikin kusoshin jami’iyar APC da suka halarci taron, ya kuma ce gwamnatinsu ta yi rawar gani dalili kenan da suke bukata a sake zabenta. Yace an samu ci gaba a gyarar hanyoyi da tsaro da ma tattalin arzikin da saransu.

More News

Qatar za ta taimaki marayu a Najeriya

Gwamnatin kasar Qatar ta bayyana cewa za ta ba da tallafi ga yara marayu sama da 1,000 da suka rasa iyayensu saboda rikicin Boko...

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma’aikatar kudin jihar ta miƙata bayanan bashin da El-Rufai ya ciwo

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma'aikatar kudi ta jihar da ta miƙa mata cikakken bayani kan basukan  da gwamnatin tsohon gwamnan jihar, Nasiru...

An dakatar da ayyukan kamfanin jiragen sama na Dana Air

Festus Keyamo, ministan harkokin sufurin jiragen sama ya umarci hukumar FAAN dake lura da sufurin jiragen sama a Najeriya ta dakatar da ayyukan kamfanin...

Yahaya Bello Ya Bayyana Dalilan Da Ya Hana Shi Bayyana A Gaban Kotu

Tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello ya ce tsoron kamun  hukumar EFCC dake yaƙi da yiwa tattalin arzikin ƙasa ne ya hana shi bayyana...