Aisha Buhari ta caccaki mai magana da yawun Buhari | BBC Hausa

Aisha Buhari

Mai dakin shugaba Muhammadu Buhari, Aisha Buhari ta wallafa wani rubutu da yake ta karakaina a shafukan sada zumunta, inda da kanta ta caccaki mai magana da yawun Buhari, malam Garba Shehu.

Rubutun da aka wallafa mai taken “Garba Shehu na wuce gona da iri”, mai dakin shugaba Buharin ta nuna yadda mai magana da yawun mijin nata ke ‘yi wa iyalan shugaban zagon kasa’.

Aisha Buhari ta ce “Garba Shehu na daya daga cikin masu kware wa Buhari baya kasancewar yaron abokin hamayyar Buharin ne a zaben shugaban kasa, Alhaji Abubakar.”

Ta kuma yi zargin Garba Shehu da yin sama da fadi da wasu kudaden ‘yan jaridu a fadar shugaban kasa.

Har wa yau, Aisha Buhari ta nuna rashin jin dadinta dangane da yadda Garba Shehu yaki cewa uffan a lokacin da ake yada jita-jitan auren Buhari da minista Sadiya Farouk.

Aisha Buhari ta kuma zargi Garba Shehu da hannu wajen dakatar da dan jaridar gidan Talbijin na NTA, Aliyu Kabir da ma’aikatar ta yi masa kan wata hira da aka yi zargin shi ya yi wa matar shugaban kasar.

To sai dai da BBC ta tuntubi Malam Garba Shehu kan batun, ya ce ba zai sa-in-sa da mai dakin mutumin da yake yi wa aiki ba.

More News

Yan bindiga sun harbi dalibai uku a Nasarawa

Dalibai uku na kwalejin kimiya da fasaha ta jihar Nasarawa ne suka jikkata a wani hari da yan bindiga suka kai. Mai magana da yawun...

Gobara ta kama wani sashe na kotun ƙolin Najeriya

An samu tashin gobara a wani sashe na Kotun Kolin Najeriya dake birnin tarayya Abuja. Kawo yanzu babu wani bayani kan musabbabin tashin gobarar amma...

Yan bindiga sun sace kwamishinan yaÉ—a labarai na Benue

Yan bindiga sun yi garkuwa da, Matthew Abo Kwamishinan Yada Labarai, Al'adu da Yawon Bude Ido na jihar Benue. An yi garkuwa da Abo a...

Nan bada jimawa za a kawo karshen rashin wutar lantarki a Kebbi

Gwamnatin jihar Kebbi ta roki mazauna jihar da su kara hakuri inda ta ce rashin wutar lantarki da ake fuskanta a jihar zai zo...