Adam A. Zango ya ce shi ne Bahaushen da ya fi kowa suna a duniya

Adam Zango
Hakkin mallakar hoto
Adam A Zango

Fitaccen jarumin fina-finan Hausa, Adam A. Zango ya koda kansa a matsayin wanda ya fi yin fice cikin hausawa a duniya.

A wasu jerin bidiyo da ya wallafa a shafin Instagram ya ce “Ni ne Bahaushen da na fi ko wane Bahaushe suna da masoya a duniya.”

Jarumin ya ce ba shi ya fada ba masu bincike ne suka binciko.

Sai dai bai bayyana wadanda suka yi binciken ba har suka tabbatar da ya fi sauran hausawa shahara a duniya.

Adam A Zango yana da mabiya dubu 891 a shafin Instagram, sai dai kuma fitaccen jarumin fina-finan hausa Ali Nuhu ya fi shi yawan mabiya a Instagram inda yake da mabiya sama da miliyan daya.

Haka ma fitacciyar jarumar finafinan Hausa Rahama Sadau ta fi shi yawan mabiya a Instagram inda take da masoya miliyan 1.2.

Amma a cikin bidiyon wanda ya kira sako ga masoyansa, A. Zango ya ce shi ne ma’anar sarki.

“Duk mutumin da yake son ya zama kamar Zango to sai ya shirya wa kalubale da gwagwarmaya, bala’i da masifa ko wane iri”

“Ni kai na da Allah ya nuna min irin matsaloli da bala’in da na shiga kafin na kai wannan matsayin to da zan hakura,” in ji shi.

Jarumin ya yi gugan zana inda ya ce kada wasu su tsargu da abin da yake fada.

Ya ce ana gayyatarsa a kasashe da dama kuma sai an rasa shi ake neman wasu saboda daukakarsa.

Rayuwar Adam A Zano a takaice

Hakkin mallakar hoto
Adam Zango
  • An haife shi a garin Zangon Kataf a jihar Kaduna
  • Ya bar garin a 1992 bayan rikicin kabilancin da aka yi
  • Ya koma arayuwa a jihar Plateau inda ya yi karatun Firamare
  • Talauci ya hana shi cigaba da karatu a wancan lokacin
  • Tun yana yaro ake masa lakabi da Usher – mawakin nan dan Amurka saboda yadda yake rawa
  • Ya koma Kano inda ya fara aiki a wani kamfanin kade-kade da raye-raye
  • Fim dinsa na farko shi ne Sirfani, wanda ya ce shi ya shirya shi da kansa
  • Ya fito a fim sama da 100 a tsawon shekara 16

More News

Mutane uku sun mutu a ruftawar wani ginin bene a Kano

Hukumar Bada Agajin Gaggawa Ta Ƙasa NEMA ta tabbatar da mutuwar mutane uku bayan da wani bene mai hawa uku ya ruguzo a unguwar...

Ganduje Ya Zargi Gwamnatin Kano Da Shirya Zanga-Zangar Neman A Sauke Shi

Shugaban jam'iyar APC na ƙasa, Abdullahi Umar Ganduje ya ce gwamnatin jihar Kano ta jam'iyar NNPP ita ce ke da alhakin shirya zanga-zanga iri...

Qatar za ta taimaki marayu a Najeriya

Gwamnatin kasar Qatar ta bayyana cewa za ta ba da tallafi ga yara marayu sama da 1,000 da suka rasa iyayensu saboda rikicin Boko...

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma’aikatar kudin jihar ta miƙata bayanan bashin da El-Rufai ya ciwo

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma'aikatar kudi ta jihar da ta miƙa mata cikakken bayani kan basukan  da gwamnatin tsohon gwamnan jihar, Nasiru...