Zababbun hotuna daga fadin Afirka, da ‘yan Afirka a wasu sassan duniya a wannan makon:
Hakkin mallakar hoto
EPA
Image caption
An fara yakin neman zaben shugaban kasa ka’in da na’in a Tunisiya kuma an dauki wata mata ranar Juma’a tana tafiya a gefen wani bango da ke dauke da fastocin ‘yan takara a Tuni, babban birnin kasar.
Hakkin mallakar hoto
EPA
Image caption
A cikin rangadin da yake yi a yankin kudancin Afirka, Fafaroma Francis ya samu tarba daga wadannan ‘yan rawar ranar Juma’a a wani filin wasa a Maputo, babban birnin Mozambique
Hakkin mallakar hoto
EPA
Image caption
Washegari fafaroman ya je Madagascar inda aka tarbe shi a babban birnin kasar Antananarivo.
Hakkin mallakar hoto
AFP
Image caption
A lokacin da labarin mutuwar Mugabe ya fara yaduwa, wata mata a Nairobi, babban birnin Kenya na kallon halin da ake ciki a wani shagon siyar da talabijin.
Hakkin mallakar hoto
Reuters
Image caption
Masu alhini sun jeru don shiga filin wasa a Harare babban birnin Zimbabwe inda za a ajiye gawar Mugabe.
Hakkin mallakar hoto
Getty Images
Image caption
‘Yar Masar Giana Lotfy (a hagu) na fafatawa da Leila Heurtault ‘yar Faransa a gasar dambe a Japan ranar Lahadi.
Hakkin mallakar hoto
Reuters
Image caption
Nan kuma dan wasan kwando na Najeriya ne Ekpe Udoh ya jefa kwallo a gasar kwallon kwando ta duniya a China.
Hakkin mallakar hoto
AFP
Image caption
A Malawi, zabaya masu shiga gasar kyau na shiri kafin fara gasar a Lilongwe.
Hakkin mallakar hoto
AFP
Image caption
Wasu mata uku a Afirka ta Kudu na shakatawa ranar Litinin a wata cibiya da ke bai wa wadanda rikicin kin jinin baki ya shafa mafaka a birnin Johannesburg…
Hakkin mallakar hoto
AFP
Image caption
Wani dan Najeriya na rera taken kasar a filin jirgin Legas a daren Laraba inda jirgi ya sauke ‘yan Najeriyar da suka tsere wa tashin hankali a Afirka ta Kudu.
Hakkin mallakar hoto
EPA
Image caption
Masu sayar da kifi a birnin Alexandria na kasar Masar sun baje hajarsu a kasuwar ranar Lahadi.
Duka hotunan na da hakkin mallaka.