Abba Gida-Gida Ya Koka Kan Rashin Ingancin Abincin Buɗa Baki Da Gwamnati Ke Rabawa

Gwamnan jihar Kano, Engr Abba Kabir Yusuf ya koka kan yadda ake sarrafawa tare da raba abincin ciyarwar watan Azumi a jihar da gwamnatin Kano ta samar.

A yayin wata ziyarar bazata zuwa ɗaya daga cikin cibiyoyin da ake dafawa tare da raba abincin dake ƙaramar hukumar Municipal gwamnan ya nuna rashin gamsuwarsa kan irin abinci da ake dafawa ake bawa jama’a.

Ya yi zargin ana zagon ƙasa a shirin inda ya ɗora ayar tambaya kan yawa a da kuma ingancin abincin da ya gani ba kamar wanda gwamnati ta amince a bayar ba.

Gwamnan ya gargadi masu dafa abinci dama wanda ya basu aikin da kada su kuskura su sake dafa makamancinsa.

Gwamna Yusuf ya umarci shugaban ma’aikatansa Shehu Wada Sagagi da ya sa ido kan yadda shirin ke gudana tare da bashi rahoton cigaban da ake samu a kullum.

More News

Mutane uku sun mutu a ruftawar wani ginin bene a Kano

Hukumar Bada Agajin Gaggawa Ta Ƙasa NEMA ta tabbatar da mutuwar mutane uku bayan da wani bene mai hawa uku ya ruguzo a unguwar...

Ganduje Ya Zargi Gwamnatin Kano Da Shirya Zanga-Zangar Neman A Sauke Shi

Shugaban jam'iyar APC na ƙasa, Abdullahi Umar Ganduje ya ce gwamnatin jihar Kano ta jam'iyar NNPP ita ce ke da alhakin shirya zanga-zanga iri...

Qatar za ta taimaki marayu a Najeriya

Gwamnatin kasar Qatar ta bayyana cewa za ta ba da tallafi ga yara marayu sama da 1,000 da suka rasa iyayensu saboda rikicin Boko...

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma’aikatar kudin jihar ta miƙata bayanan bashin da El-Rufai ya ciwo

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma'aikatar kudi ta jihar da ta miƙa mata cikakken bayani kan basukan  da gwamnatin tsohon gwamnan jihar, Nasiru...