Alkalin Alkalan Najeriya zai gurfana a kotu saboda kin bayyana kadarorinsa

Gwamnatin Najeriya ta bukaci Alkalin alkalan
kasar mai sharia Walter Onnoghen ya tsayar da
aikinsa kan zargin da yake da nasaba da kin bayyana
kadarorin da ya mallaka.

Wata sanarwa daga kotun da’ar ma’aikata, ta ce
a ranar Litinin 14 ga watan Janairu, Alkalin alkalan zai gurfana gabanta a wani mataki da ake ganin na kokarin tube shi daga mukaminsa. Jami’in hulda da jama’a na kotun da’ar ma’aikata, Ibraheem Al-Hassan, ya tabbatar wa da manema labaru da shari’ar da za a soma ta Alkalin alkalan.

Ana sa ran kotun da zai gurfana ita ce za ta tube shi daga mukaminsa domin kada ya yi katsalandan ga shari’ar.

Laifuka shida ake tuhumarsa, dukkaninsu da suka shafi kin bayyana dukiyar da ya mallaka.
Gwamnatin tarayya dai na zarginsa ne da saba wa dokar hukumar tabbatar da da’a ta Code of Conduct Bureau.

Rahotanni sun ce tun a ranar Juma’a aka sanar da shi kan lafiukan da ake zarginsa da kuma bukatar ya gurfana gaban kotu a ranar Litinin.

More from this stream

Recomended

Kotun Tarayya Ta Tabbatar Da David Mark A Matsayin Shugaban ADC

Wata babbar kotun tarayya da ke Abuja ta tabbatar da shugabancin jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) Æ™arÆ™ashin jagorancin tsohon shugaban majalisar dattawa, David Mark. Kotun ta yi watsi da Æ™arar da É—an majalisar wakilai, Leke Abejide, ya shigar kan shugabancin jam’iyyar, inda ta bayyana cewa lamarin ya shafi harkokin cikin gida na jam’iyyar siyasa. Mai […]