Alkalin Alkalan Najeriya zai gurfana a kotu saboda kin bayyana kadarorinsa

Gwamnatin Najeriya ta bukaci Alkalin alkalan
kasar mai sharia Walter Onnoghen ya tsayar da
aikinsa kan zargin da yake da nasaba da kin bayyana
kadarorin da ya mallaka.

Wata sanarwa daga kotun da’ar ma’aikata, ta ce
a ranar Litinin 14 ga watan Janairu, Alkalin alkalan zai gurfana gabanta a wani mataki da ake ganin na kokarin tube shi daga mukaminsa. Jami’in hulda da jama’a na kotun da’ar ma’aikata, Ibraheem Al-Hassan, ya tabbatar wa da manema labaru da shari’ar da za a soma ta Alkalin alkalan.

Ana sa ran kotun da zai gurfana ita ce za ta tube shi daga mukaminsa domin kada ya yi katsalandan ga shari’ar.

Laifuka shida ake tuhumarsa, dukkaninsu da suka shafi kin bayyana dukiyar da ya mallaka.
Gwamnatin tarayya dai na zarginsa ne da saba wa dokar hukumar tabbatar da da’a ta Code of Conduct Bureau.

Rahotanni sun ce tun a ranar Juma’a aka sanar da shi kan lafiukan da ake zarginsa da kuma bukatar ya gurfana gaban kotu a ranar Litinin.

More News

Najeriya za ta dena shigo da man fetur a cikin watan Yuni – Dangote

Aliko Dangote mutumin da ya fi kowa arziki a Nahiyar Afirka ya ce Najeriya za ta daina shigo da man fetur a cikin watan...

An ceto mutane 9 daga wani ginin bene da ya ruguzo a jihar Niger

Mutane 9 aka samu nasarar cetowa daga wani ginin bene mai hawa É—aya da ya ruguzo a yankin Sabon Gwari dake garin Minna babban...

An yi faÉ—a tsakanin masu sayar da waya da sojoji a kasuwar Abuja

Rundunar ‘yan sandan babban birnin tarayya, ta tura jami’an leken asiri zuwa kasuwar Banex – wata kasuwar kayan lantarki da na’urorin sadarwa da ke...

Yawan Mutanen Da Suka Mutu A Wutar Da Wani Matashi Ya Cinnawa Wani Masallaci A Kano Sun  Karu Zuwa 16

Rundunar ƴan sandan jihar Kano ta ce yawan mutanen da suka mutu sakamakon wutar da wani ya cinnawa wani masallaci a ƙauyen Gadan a...