Iyalan Mutanen Da Aka Sace A Kwara Sun Ce Masu Garkuwa Sun Ki Karɓar Kuɗin Fansa Ta Naira Miliyan 155



Iyalan mutanen da aka sace a harin da aka kai ƙauyukan Woro da Nuku da ke karamar hukumar Kaiama a Jihar Kwara sun ce masu garkuwa da mutanen sun ƙi karɓar kuɗin fansa na N155 miliyan da suka tara domin a sako ‘yan uwansu.

Da yake zantawa da BBC Hausa, Alhaji Abdul Ibrahim, wanda ya wakilci iyalan da abin ya shafa, ya ce ya rasa ‘yan uwa 10 a harin, yayin da har yanzu mutum 35 daga cikin iyalansa ke hannun masu garkuwa.

Ya ce sun kai kuɗin fansar kamar yadda aka buƙata, amma masu garkuwar sun ƙi karɓa saboda sun ce bai isa ba. Tun daga lokacin kuma ba su sake jin labarin waɗanda aka sace ba.

Iyalan sun yi kira ga Gwamnatin Tarayya da Gwamnatin Jihar Kwara da su gaggauta ceto mutanen, suna mai cewa sun yi iya ƙoƙarinsu amma abin ya fi ƙarfinsu.

Harin, wanda ya faru a ranar 3 ga Fabrairu, 2026, ya yi sanadin mutuwar sama da mutum 260, ƙone gidaje sama da 30 da kuma sace mutum 176, a cewar shugabannin al’umma. A halin yanzu, ɗan majalisar dokokin jihar mai wakiltar yankin ya kuma buƙaci gwamnati ta ƙara ƙaimi wajen ceto waɗanda har yanzu suke tsare.

More from this stream

Recomended