Fadar Shugaban Ƙasa Ta Zargi Wani Mutum Da Samar Da Wata Ma’aikatar Gwamnati Ta Bogi

Fadar shugaban ƙasa ta zargi Adeyemi Adeniyi Mathew da kasancewa ɗan damfara da ya naɗa kansa shugaban wata hukumar neman tallafi daga ƙasashen waje tare da buɗe ofis a ginin Sakatariyar Gwamnatin Tarayya.

Adeyemi ya yi ikirarin cewa mai bai wa shugaban ma’aikatan fadar shugaban ƙasa shawara ne ya naɗa shi a mukamin, amma shugaban ma’aikatan fadar shugaban ƙasa, Femi Gbajabiamila, ya musanta wannan zargi.

Gwamnatin tarayya ta kuma buƙaci ‘yan ƙasa da su guji yaɗa jita-jita ko yin shaci-faɗi kan lamarin, tana mai cewa batun yana gaban kotu domin ci gaba da shari’a.

More from this stream

Recomended

Kotun Tarayya Ta Tabbatar Da David Mark A Matsayin Shugaban ADC

Wata babbar kotun tarayya da ke Abuja ta tabbatar da shugabancin jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) ƙarƙashin jagorancin tsohon shugaban majalisar dattawa, David Mark. Kotun ta yi watsi da ƙarar da ɗan majalisar wakilai, Leke Abejide, ya shigar kan shugabancin jam’iyyar, inda ta bayyana cewa lamarin ya shafi harkokin cikin gida na jam’iyyar siyasa. Mai […]