An Jibge Jami’an Tsaro Yayin Da Zanga-Zangar Kyamar Baƙi Ke Ci Gaba A Afirka Ta Kudu



Ana ci gaba da gudanar da zanga-zangar kyamar baƙi a wasu sassan Afirka ta Kudu, lamarin da ya sa hukumomi suka jibge jami’an tsaro saboda fargabar barkewar rikice-rikice.

Shugaban ƙasar, Cyril Ramaphosa, ya bukaci masu zanga-zangar su guji tashin hankali tare da gudanar da zanga-zangar cikin lumana ba tare da tsoratar da jama’a ba.

Zanga-zangar na da nasaba da wa’adin da wasu ƙungiyoyi suka bai wa baƙin da ba su da takardun izinin zama a kasar su fice.

Lamarin ya haddasa fargaba tsakanin baki ‘yan Afirka da ke zaune a Afirka ta Kudu, yayin da wasu kasashe ke ci gaba da bibiyar halin da ake ciki.

More from this stream

Recomended

Kotun Tarayya Ta Tabbatar Da David Mark A Matsayin Shugaban ADC

Wata babbar kotun tarayya da ke Abuja ta tabbatar da shugabancin jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) ƙarƙashin jagorancin tsohon shugaban majalisar dattawa, David Mark. Kotun ta yi watsi da ƙarar da ɗan majalisar wakilai, Leke Abejide, ya shigar kan shugabancin jam’iyyar, inda ta bayyana cewa lamarin ya shafi harkokin cikin gida na jam’iyyar siyasa. Mai […]