Kungiyar masu fafutukar kafa kasar Biafra ta IPOB ta sanar da dakatar da ofishin jagoranta Nnamdi Kanu da kuma ofishin Daraktan Radio Biafra.
Sanarwar ta fito ne bayan taron shugabannin kungiyar da aka gudanar ranar Laraba. Shugaban Directorate of State, Mazi Chikadibia Edoziem, ya ce an dauki matakin ne bayan nazarin wasu rahotannin sirri da suka shafi sakonnin da ake zargin an aika daga gidan yarin Sokoto.
Kungiyar ta bayyana cewa Directorate of State ne zai ci gaba da kula da harkokin IPOB da kuma tafiyar da ayyukanta.
IPOB ta ce an kafa kungiyar ne ta hannun ’yan Biafra mazauna kasashen waje, ba mutum guda ba. Ta kuma jaddada cewa babu wanda yake da ikon rusa Directorate of State.
Kungiyar ta kara da cewa wasu kalamai da sakonni daga gidan yarin Sokoto sun haddasa kama mambobinta da mutuwar wasu a yankin Biafra.
Haka kuma IPOB ta nuna damuwa kan zargin yunkurin kafa wata kungiyar daukar makamai da ka iya jawo sabon rikici a Kudu maso Gabashin Najeriya.
IPOB Ta Dakatar Da Ofishin Nnamdi Kanu

