Mutum Ɗaya Ya Mutu A Harin Da Aka Kai Filin Jirgin Sama Na Kuwait



Aƙalla mutum ɗaya ya rasa ransa, yayin da wasu sittin da uku suka jikkata bayan wani jirgi mara matuƙi da Iran ake zargi ya kai hari a tashar fasinjoji ta Filin Jirgin Sama na Ƙasa da Ƙasa na Kuwait.

Mahukuntan Indiya sun tabbatar da cewa mamacin ɗan ƙasarsu ne, yayin da wasu ‘yan ƙasar ma suka samu raunuka a harin.

Sojojin Kuwait sun yi Allah-wadai da lamarin, inda suka bayyana shi a matsayin harin ta’addanci daga Iran. Sai dai dakarun kare juyin juya halin Iran sun zargi Amurka da haddasa sabon tashin hankalin, bayan hare-haren da suka ce an kai a wasu wurare a Iran.

Ma’aikatar Lafiya ta Kuwait ta ce mutum sittin da uku sun samu kulawar likitoci sakamakon raunukan da suka samu.

Bayan harin, hukumomin Kuwait sun dakatar da zirga-zirgar jiragen sama na ɗan lokaci tare da karkatar da wasu jirage zuwa wasu filayen jiragen sama. Daga baya an dawo da ayyukan zirga-zirgar jiragen.

Rahotanni sun ce Kuwait ta gano makamai masu linzami da jirage marasa matuƙi kusan talatin da aka harba yayin harin. Haka kuma Bahrain ta ba da rahoton wasu hare-haren jirage marasa matuƙi, yayin da Hadaddiyar Daular Larabawa ta yi kira ga ƙasashen yankin su haɗa kai wajen tunkarar matsalar.

Sabon tashin hankalin ya ƙara jefa yankin Gulf cikin damuwa, tare da haifar da fargabar cewa yarjejeniyar tsagaita wutar da aka cimma a baya za ta iya rushewa.

More from this stream

Recomended