Iran Ta Gargadi Amurka Da Isra’ila Kan Sake Kai Mata Hari



Rundunar Juyin Juya Halin Iran ta yi gargaɗin cewa duk wani sabon hari da Amurka ko Isra’ila za su kai wa Iran zai iya haddasa faɗaɗa rikici fiye da yankin Gabas ta Tsakiya.

A wata sanarwa da rundunar ta fitar, ta ce duk wani farmaki kan Iran zai fuskanci martani mai tsanani, bayan barazanar sake kai hari da shugaban Amurka Donald Trump da wasu jami’an Isra’ila suka yi.

Haka kuma, ministan harkokin wajen Iran, Abbas Araghchi, ya bayyana cewa ƙasarsa ta ƙara ƙwarewa da kuma koyo daga abubuwan da suka faru a baya, yana mai cewa Amurka za ta “ga abin mamaki” idan aka sake kai wa Iran hari.

A gefe guda, Trump ya bayyana cewa ya taba dakatar da wani harin soji kan Iran a lokacin da ake shirin kai shi, bayan roƙon wasu shugabannin yankin.

More from this stream

Recomended