Ƴan Bindiga Sun Sake Sanya Harajin Naira Miliyan 10 A Katsina



Rahotanni daga jihar Katsina sun bayyana cewa wasu ’yan bindiga sun sanya sabon haraji na Naira miliyan 10 a kan kowace daga cikin al’ummomin Garin Lamido da Yan Shuni da ke ƙaramar hukumar Bakori.

An ce waɗannan ’yan bindiga suna biyayya ga wani shahararren jagoran su mai suna Isiya Kwashen Garwa.

Lamarin ya faru ne duk da yarjejeniyoyin sulhu da aka yi a baya tsakanin hukumomi, shugabannin al’umma da wakilan ’yan bindiga a yankin.

Wani mai sharhi kan harkokin tsaro, Bakastine, ne ya bayyana hakan a shafinsa na X, inda ya nuna damuwa kan halin da yankunan karkara ke ciki.

Rahotanni sun nuna cewa wannan sabon haraji ya haifar da fargaba sosai a tsakanin mazauna yankin, inda wasu iyalai suka bar gidajensu don tsoron farmaki.

Mazauna yankin sun bayyana rashin jin daɗi kan yadda ake maimaita yarjejeniyoyin sulhu ba tare da dorewar zaman lafiya ba.

More from this stream

Recomended