
Gwamnatin jihar Cross Rivers ta ce ta gano tare da killace wasu mutane 10 da suka yi mu’amala da dan ƙasar China da ya sake shigo da cutar Covid-19 Najeriya.
Da take magana da jaridar Daily Trust babbar jami’ar jihar dake lura da cututtuka masu yaɗuwa ta ce an gano mutanen ne a lokacin da jami’an kiwon lafiya su ka bi diddigin mutanen da ya yi cuɗanya da su.
Ta ce tawagarta sun ziyarci wurin aikin mutumin dake karamar hukumar Akamkpa ta jihar.
Ekpenyong ta kara da cewa a yanzu haka marar lafiyar yana murmurewa a Asibitin Koyarwa na Jami’ar Calabar.

