
Ƴan majalisar wakilai ta tarayya 3 sun koma jam’iyar ADC gabanin zaɓen shekarar 2027.
Thaddeus Attah dake wakiltar mazaɓar Eti-Osa ta jihar Lagos ƙarƙashin jam’iyar LP, Usman Zubairu mazaɓar Birnin Gwari/Giwa a jihar Kaduna karkashin jam’iyar APC da kuma Sani Noma dake wakiltar mazaɓar Argungu/Augie a jihar Kebbi karkashin jam’iyar PDP na daga cikin ƴan majalisar da suka koma jam’iyar ADC.
A jihar Niger dan majalisar wakilai ta tarayya, Abubakar Buba dake wakiltar mazaɓar Chanchangi da kuma Ibrahim Mohammed dake wakiltar mazaɓar Bunza/Birnin Kebbi/Kalgo sun fice daga jam’iyarsu ta PDP ya zuwa APC.
Daga jihar Osun dan majalisar wakilai Mudashiru Alani da Adetunji Olusoji sun fice daga jam’iyar PDP ya zuwa jam’iyar Accord Party.
Daga jihar Taraba dan majalisar wakilai, David Fuoh ya fice daga jam’iyar APC ya zuwa PDP
A wasikar da ya karanta mataimakin shugaban majalisar Benjamin Kalu dukkanin yan majalisar sun alaƙanta sauya shekar da irici

