
Jam’iyar NNPP ta zaɓi, Bala Mohammed a matsayin sabon shugaban jam’iyyar na kasa.
Zaɓen nasa na zuwa ne bayan da shugaban jam’iyar, Ajuji Ahmad wanda aka naɗa shugabancin riko a watan Maris na shekarar 2024 ya sanar da yin murabus.
A wata sanarwa ranar Lahadi, Ladipo Johnson mai magana da yawun jam’iyar na kasa ya ce yan kwanaki da su ka wuce ne Ahmad ya koma jam’iyyar ADC
Johnson ya bayyana cewa Muhammad wanda ya fito daga jihar Kaduna shi ne sakataren tsare-tsare na jam’iyar kuma kwararre wajen gudanar da mulki.

