
Daruruwan matasa ne a ƙarƙashin ƙungiyar Coalition for Jonathan Goodluck Jonathan su ka tattara a kofar gidan tsohon shugaban ƙasa Goodluck Jonathan inda suka shawarce shi da ya tsaya takarar shugaban ƙasa a zaɓen shekarar 2027.
Taron dandazon matasan ya jawo cunkoson ababen hawa a yankin a dai-dai lokacin da suka riƙa rera wakoki tare daga alluna dake dauke da rubutun kiran tsohon shugaban kasar ya tsaya takara.
Wasu daga cikin allunan an rubuta: ” GEJ Najeriya tana durƙushewa ka ceto ta”, ” GEJ matasan Najeriya sun karya asirin da aka yi maka.” da sauransu kalamai iri-iri.
Tom Ohikere shugaban kungiyar na ƙasa wanda tsohon kwamishina ne a jihar Kogi shi ne wanda ya jagoranci taron gangamin.
Ohikere ya ce sai da suka zagaya sassan Najeriya baki ɗaya kafin domin tuntuba tare da jin ra’ayoyin jama’a kafin su gudanar da taron gangamin a gidan tsohon shugaban kasar.
Sai dai har ya zuwa lokacin da su ka watse daga wurin ba a ga keyar Jonathan ba ko kuma wani daga cikin wakilansa. Amma Ohikere ya ci alwashin cigaba da gudanar da taron gangamin har sai Jonathan ya saurare su.

