Tinubu Ya Bukaci Gwamnoni Su Rage Tasirin Tsadar Mai, Yayin Da Ake Tattauna Batun ‘Yan Sandan Jihohi

Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya buƙaci gwamnonin jihohi da su ƙirƙiri matakai domin rage raɗaɗin hauhawar farashin man fetur ga al’umma. Ya ce ya dace a mayar da hankali kan fannoni kamar makamashi da sufuri, tare da ƙara tallafawa marasa ƙarfi a cikin al’umma.

A nasa ɓangaren, shugaban ƙungiyar gwamnonin Najeriya kuma gwamnan jihar Kwara, AbdulRahman AbdulRazaq, ya yaba da ƙoƙarin shugaban ƙasa. Ya ce gwamnonin za su ci gaba da aiki tare domin kawo ƙarshen matsalar tsaro a ƙasar.

Haka kuma, ya bayyana cewa ana ci gaba da tattaunawa kan batun kafa ‘yan sandan jihohi, tare da shirin kai wannan batu gaban majalisar dokoki domin samar da doka mai ɗorewa.

More from this stream

Recomended