Makami Mai Linzami Ya Lalata Makarantar Yara A Tsakiyar Isra’ila

Kafofin yaɗa labaran Isra’ila sun ruwaito cewa wani makami mai linzami mai ƴaƴa ya jawo ɓarna a wata makarantar renon yara da ke Rishon Lezion a tsakiyar ƙasar.

Rahotanni sun ce tarkacen makamin ne ya lalata wani ɓangare na ginin makarantar, ba tare da ya bugi ginin kai tsaye ba.

An kuma bayyana cewa wasu gungun alburusai sun tarwatse a cikin iska bayan an harba su, lamarin da ya sa ƙananan bama-bamai suka watse a kan wani yanki mai faɗi.

A halin yanzu, rundunar tsaron cikin gida ta Isra’ila na ci gaba da gudanar da ayyukan ceto da bincike a wurare daban-daban da abin ya shafa a yankin tsakiyar ƙasar.

More from this stream

Recomended