
Babban sifetan yan sandan Najeriya, Tunde Disu ya ziyarci mutanen da su ka jikkata a harin bom da aka kai birnin Maiduguri a ranar Litinin.
Rundunar ƴan sandan jihar Borno ta tabbatar da mutuwar mutane 23 a yayin da wasu 108 su ka jikkata a lokacin harin bom din a wasu wurare uku dake birnin.
An kai harin ne da misalin 07:24 na daren ranar Litinin a wurare uku da su ka hada da babbar kasuwar Maiduguri , kofar shiga asibitin koyarwa na Jami’ar Maiduguri da kuma gadar sama ta Post Office.
A cewar Zagazola Makama dake wallafa bayanai kan sha’anin tsaro a yankin tafkin Chadi, Disu ya ziyarci Asibitin Koyarwa na Jami’ar Maiduguri inda ake kula da mutanen da harin bom din ya shafa.
Ya gana da waɗanda su ka jikkata da kuma yan uwansu da ya yi musu jaje ya kuma tabbatar musu cewa jami’an tsaro suna aiki tukuru domin gano tare da kassara mutanen dake da hannu a harin.
Babban sifetan ya kuma ziyarci kasuwar Monday Market wacce ke daya daga cikin wurin da aka kawo harin domin dubawa halin da ake ciki.

