Tinubu Ya Umarci Hafsoshin Tsaro Su Koma Maiduguri Bayan Harin Bama-Bamai

Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, ya umarci manyan hafsoshin tsaron ƙasar da su gaggauta komawa birnin Maiduguri na jihar Borno, bayan harin bama-bamai da ya yi sanadin mutuwar aƙalla mutum 23 a ranar Litinin.

Shugaban ya yi Allah-wadai da hare-haren, inda ya bayyana su a matsayin muggan ayyukan ‘yan ta’adda da ke ƙoƙarin sanya tsoro a zukatan al’umma.

Jami’ai sun bayyana cewa fashewar bama-baman ta faru ne bayan da sojoji suka dakile wani hari da wasu da ake zargin mayaƙan ƙungiyar IS ne suka kai a wani sansanin soji da ke kusa da Maiduguri.

A halin da ake ciki, rundunar sojin Najeriya ta yi gargaɗin yiwuwar ƙaruwa hare-hare a yankin arewa maso gabas, musamman a wannan lokaci na ƙarshen watan Ramadan.

More from this stream

Recomended