
Gwamnatin jihar Adamawa ta saka dokar hana fita ta tsawon sa’o’i 24 a karamar hukumar Lamurde biyo bayan rikici a tsakanin al’ummomin Chobo da Bachawa.
A wata sanarwa ranar Lahadi, Mr Humwashi Wonosikou mai magana da yawun gwamnan jihar, Ahmadu Fintiri ya ce gwamnatin ba za ta zuba ido wasu batagari suna tayar da rikici tare da kawo rashin zaman lafiya a jihar.
“Gwamnan jihar Adamawa, Ahmadu Fintiri ya saka dokar hana fita ta tsawon sa’o’i 24 a karamar hukumar Lamurde da ba tare da bata lokaci ba. Hakan ya biyo bayan sabon farmaki da ya haifar da rashin zaman lafiya a wasu garuruwa, ” a cewar sanarwar.
Sanarwar ta kara da cewa an umarci jami’an tsaro da su tabbatar an bi dokar sau da kafa wacce za ta ji gaba da aiki har sai gwamnati ta fitar da wata sanarwa anan gaba.
Gwamnati ta shawarci mazauna wuraren da su tabbatar sun bi dokar tare da bawa jami’an tsaro bayanai domin a samu tabbatar da zaman lafiya.
Sanarwar ta yi gargadin cewa duk wanda aka samu yana karya dokar hana fitar za a kama shi tare da hukunta shi.

