Dakarun Juyin Juya Halin Iran (IRGC) sun bayyana cewa sun kai harin “manyan makamai” masu linzami kan wani sansanin sojin Amurka da ke ƙasar Bahrain.
IRGC ta ce harin ya zo ne a matsayin martani ga wasu rahotanni da ke cewa Amurka ta kai hari a wata cibiyar tace ruwan sha da ke wani tsibiri a mashigin Hormuz, duk da cewa ba a tabbatar da rahoton ba.
A cikin wata sanarwa da rundunar ta fitar ta hanyar kafar yaɗa labaran Fars, wadda ke da alaƙa da IRGC, rundunar ta ce: “A matsayin martani ga harin da Amurka ta kai daga sansanin Juffair a kan tashar Qeshm, wannan sansanin na Amurka ya fuskanci mummunan hari daga rundunar IGRC.”
A halin da ake ciki, an ji ƙarar sautin na’urorin ankararwa a sassa daban-daban na Bahrain. Ma’aikatar harkokin cikin gida ta ƙasar ta buƙaci ‘yan ƙasa da mazauna yankin su nemi mafaka a wuraren ɓuya masu aminci.
Rahotanni sun ce ma’aikatar cikin gidan Bahrain ta wallafa a shafinta na X cewa an samu tashin gobara da ƙonewar wasu gine-gine a Manama, babban birnin ƙasar.
Ta ce jami’an kashe gobara suna aiki domin shawo kan wutar.
IRGC Ta Ce Ta Kai Harin Makamai Masu Linzami Kan Sansanin Sojin Amurka A Bahrain

